Виберіть мову

mic

Поділіться

поділіться посиланням

QR code for https://globalrecordings.net/script/8177

unfoldingWord 30 - Yesu ya Ciyar da Mutane Dubu Biyar

unfoldingWord 30 - Yesu ya Ciyar da Mutane Dubu Biyar

абрис: Matthew 14:13-21; Mark 6:31-44; Luke 9:10-17; John 6:5-15

Номер сценарію: 1230

Мову: Hausa

Аудиторія: General

Мета: Evangelism; Teaching

Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture

Статус: Approved

Сценарії є основними вказівками для перекладу та запису на інші мови. Їх слід адаптувати, якщо це необхідно, щоб зробити їх зрозумілими та відповідними для кожної окремої культури та мови. Деякі терміни та поняття, які використовуються, можуть потребувати додаткових пояснень або навіть бути замінені чи повністю опущені.

Текст сценарію

Yesu ya aiki manzaninsa su yi wa'azi da koyarwa a kauyuka dabam-dabam masu yawa. Da suka dawo, wurin da Yesu yake, suka gaya masa abin da suka yi. Sai Yasu ya gayyace su, su je wani wuri tare da shi a kebe a ketaren tafki domin su huta a can na dan lokaci. Sai, suka shiga jirgin ruwa suka ketare zuwa gaccin tafkin.

Amma akwai mutane da yawa da suka ga Yesu da almajiran sa sun tafi a jirgin ruwan. Wadannan mutanen suka ruga suka bi bakin tafkin domin su riga su zuwa dayan tsallaken. Yayin da Yesu da almajiran sa suka isa can, taron mutane da yawa na nan suna jiran su.

Taron na da maza fiye da 5,000, ba a ma kirga mata da yara ba. Yesu ya yi juyayi kwarai game da mutanen. Ga Yesu, mutanen nan na kama suke da tumaki da basu da makiyayi. Saboda haka ya koyar da su, ya kuma warkar da wadan da suke da rashin lafiya a cikin su.

Can da yamma, almajiran suka ce wa Yesu, "Lokaci ya kure kuma ba garuruwa kusa. Ka sallami mutanen domin su je su sami abinda za su ci."

Amma Yesu ya ce wa almajiran, "Ku ba su abinda za su ci!" Suka ansa da ce wa, "Ya ya zamu yi haka? Muna da curin gurasa biyar da 'yan kifi biyu."

Yesu ya ce wa almajiran sa, su ce wa mutanen dake taron su zauna a kan ciyawa, a rukunin mutane hamsin hamsin.

Sa'annan Yesu ya dauki gurasa biyar da kifi biyun, ya duba sama, ya kuma godewa Allah domin abincin.

Sai, Yesu ya gutsuttsura gurasar da kifin. Ya ba wa almajiran sa, don su ba wa mutanen. Almajiran su ka ci gaba da mika abincin, bai kuma kare ba! Dukkan mutanen suka ci suka kuma koshi.

Bayan haka, almajiran suka tattara sauran abincin da ba'a ci ba, ya kuma isa ya cika kwanduna goma sha biyu! Dukkan abincin nan ya samu ne daga gurasa biyar da kifi biyun.

Пов'язана інформація

Слова життя - Аудіо євангельські послання тисячами мов, що містять біблійні послання про спасіння та християнське життя.

Copyright and Licensing - GRN shares its audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?