unfoldingWord 24 - Yahaya ya yi wa Yesu Baftisma
Anahat: Matthew 3; Mark 1; Luke 3; John 1:15-37
Komut Dosyası Numarası: 1224
Dil: Hausa
Kitle: General
Amaç: Evangelism; Teaching
Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture
Durum: Approved
Komut dosyaları, diğer dillere çeviri ve kayıt için temel yönergelerdir. Her bir farklı kültür ve dil için anlaşılır ve alakalı hale getirmek için gerektiği gibi uyarlanmalıdırlar. Kullanılan bazı terimler ve kavramlar daha fazla açıklamaya ihtiyaç duyabilir veya hatta tamamen değiştirilebilir veya atlanabilir.
Komut Dosyası Metni
Yahaya, 'dan Zakariya da Alisabatu, ya yi girma ya kuma zama annabi. Yayi rayuwa cikin jeji, yana cin zuma da fara, ya na kuma sanye da tufafin da aka yi da gashin rakumi.
Mutane da dama suka fito zuwa jejin domin su saurari Yahaya. Sai ya yi masu wa'azi, ya na cewa, "Ku tuba domin mulkin Allah ya kusa!"
Da mutane suka ji sakon Yahana, da yawa daga cikinsu suka tuba daga zunubansu, sai Yahaya ya yi masu baftisma. Shugabanin addini da yawa suka zo wurin Yahaya domin ya yi masu baftisma, amma basu tuba ko kuma su furta zunubansu ba.
Yahaya ya ce wa shugabanin addinin, "Ku macizai masu dafi! Ku tuba ku sake halayen ku. Duk itacen da bata bada 'ya'ya mai kyau ba, za a sare ta a jefa ta cikin wuta." Yahaya ya cika abin da annabawa suka fada, "Duba, na aiko manzo na, a yariga ka gaba, wanda zai shirya hanyar ka."
Wassu daga cikin Yahudawan suka tambayi Yahaya ko shi ne Almasihu, Yahaya kuwa ya amsa, "Bani ne Almasihun ba, amma akwai wanda ke biye da ni. Shi mai girma ne, wanda ban isa in kwance takalmansa ba.''
Kashe gari, Sai Yesu yazo domin Yahaya ya yi masa baftisma. Da Yahaya ya ganshi, sai ya ce, "Duba! Ga 'Dan Rago na Allah wanda zai kawar da zunuban duniya."
Yahaya ya ce wa Yesu, "Ban isa in yi maka baftisma ba. Maimakon haka kaine zaka yi mani baftisma.'' Amma Yesu yace, ''Kayi mani baftisma, domin abin da ya dace ne ayi." Hakanan Yahaya ya yi masa baftisma, ko da shike Yesu bai taba yin zunubi ba.
Sa'anda Yesu ya fito daga ruwa, bayan an yi masa baftisma, sai Ruhun Allah ya bayyana a misalin kurciya ya sauko a kansa. A wannan lokaci, muryar Allah yayi magana daga sama, yana cewa, "Kai 'Da na ne wanda nake kauna, ina kuma farin ciki da kai sosai."
Allah ya fadawa Yahaya, "Ruhu Mai Tsarki zai sauko kan wani wanda zaka yi masa baftisma. Wannan mutumin shi ne 'Dan Allah." Allah daya ne. Amma da Yahaya ya yi wa Yesu baftisma, ya ji Allah Uba yayi magana, ya ga Allah 'Da, shi ne Yesu, ya kuma ga Ruhu Mai Tsarki.