unfoldingWord 11 - Ketarewa
Përvijimi: Exodus 11:1-12:32
Numri i skriptit: 1211
Gjuhe: Hausa
Audienca: General
Qëllimi: Evangelism; Teaching
Veçoritë: Bible Stories; Paraphrase Scripture
Statusi: Approved
Skriptet janë udhëzime bazë për përkthimin dhe regjistrimin në gjuhë të tjera. Ato duhet të përshtaten sipas nevojës për t'i bërë të kuptueshme dhe relevante për çdo kulturë dhe gjuhë të ndryshme. Disa terma dhe koncepte të përdorura mund të kenë nevojë për më shumë shpjegime ose edhe të zëvendësohen ose të hiqen plotësisht.
Teksti i skenarit
Allah ya gargadi Fir'auna, cewa idan bai saki yayan Isra'ila su tafi ba, zai kashe dukan yan fari maza na mutane Masar da dabbobi. Da Fir'auna ya ji wannan, har yanzu ya ki ya gaskanta ya kuma yi biyaya da Allah.
Allah yayi tanadin hanyar ceton dan farin duk wanda ya gaskanta ga shi. Kowace iyali ta zabi dan rago mara lahani ta yanka
Allah ya fada wa Isra'ilawa su shafa jinin dan ragon kewaye da kofar gidansu, su gasa nama su ci agagauce tare da gurasa mara yisti. Ya kuma fada masu su shirya su bar Masar bayan sun ci
Israilawa sun yi komai kamar yadda Allah ya umurce su su yi. Da tsakar dare, Allah ya ratsa cikin Masar ya na kishan kowane dan fari.
Dukan gidajen Israilawa na shafe da jini kewaye da kofofin su, Allah ya ketare gidajen. Kowa da ke cikin su ya tsira. Sun tsira saboda jinin dan ragon
Amma Masarawa basu gaskanta Allah ko su yi biyaya da umuninsa ba. Don haka Allah bai ketare gidajensu ba, Allah ya kashe kowane daya na yayan fari maza na Masarawa.
Kowane dan fari na Masar ya mutu, daga dan farin wanda yake daure a kurkuku, zuwa dan farin Fir'auna. mutane da dama a Masar sun yi kuka da kururuwa saboda tsananin bakin ciki.
A wannan daren, Fir;auna ya kira Musa da Haruna ya ce, "Dauki Israilawa ku bar Masar nan take!" Mutanen Masar kwa suka roki Isra'ilawa su tafi nan take.