unfoldingWord 27 - Labarin Basamare Nagari
Obrys: Luke 10:25-37
Číslo skriptu: 1227
Jazyk: Hausa
publikum: General
Účel: Evangelism; Teaching
Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture
Postavenie: Approved
Skripty sú základnými usmerneniami pre preklad a nahrávanie do iných jazykov. Mali by byť podľa potreby prispôsobené, aby boli zrozumiteľné a relevantné pre každú odlišnú kultúru a jazyk. Niektoré použité termíny a koncepty môžu vyžadovať podrobnejšie vysvetlenie alebo môžu byť dokonca nahradené alebo úplne vynechané.
Text skriptu
Wata rana, wani masanin shari'ar Yahudawa, ya zo wurin Yesu domin ya gwada shi, yana cewa, "Malam, me zan yi in gaji rai madawwami?" Yesu ya amsa, "Me aka rubuta a shari'ar Allah?"
Gwanin a dokokin Allah ya ce, "Ku kaunaci Ubangiji Allahn ku da dukkan zuciyar ku, da ran ku, da karfin ku, da kuma hankalin ku. Ka kuma kaunaci, makwabcin ka kamar kanka." Yesu ya amsa, "Ka yi dai dai! Ka yi haka za ka rayu."
Amma masanin shari'ar ya so ya tabbatar shi mai adali ne, sai ya sake yin tambaya, "Wanene makwabci na?"
Yesu ya amsa wa masanin shari'ar ta wurin bada labari. "An yi wani Bayahude da yake tafiya akan hanya daga Urushalima zuwa Yariko."
“Yayin da mutumin yake tafiya, 'yan fashi suka fada masa. Suka kwace duk abin da ye ke da shi, suka kuma yi masa duka har ya kusa mutuwa. Sa'anna suka yi tafiyar su.”
“Nan da nan bayan haka, wani Firist Bayahude tafiya ta kawo shi wannan hanyar. Da wannan shugaban adini ya ga mutumin da aka yi wa duka da fashi, sai ya bi gefe daya na hanyar, ya kyale mutumin nan dake bukatar taimako, ya ci gaba da tafiya.''
"Jim kadan da yin haka, wani Balawe ya gangaro kan hanyar. (Lawiyawa sune kabilun Yahudawa wandanda ke taimakon firistoci a Haikali.) Balawen shima ya ketare gefen hanya, bai kula mutumin da haka yi wa fashi da duka ba.”
“Mutumin da ke biye akan hanyar kuwa Basamare ne. (Samariyawa sune zuriyar Yahudawa wadan da suka auri mutane daga wassu al'umma. Samariyawa da Yahudawa sun tsani juna.) Amma da Basamaren ya ga Bayahuden, ya yi juyayi domin sa. Sai ya lura da shi ya daure masa raunukansa.”
“Basamaren ya dauki mutumin nan ya sa akan jakin sa, ya kai shi wani masauki baki kusa da hanya inda ya kula da shi.”
Kashegari, Basamaren yana bukatar yaci gaba da tafiyar sa. Sai ya ba wa mai kula da masaukin kudi yace, 'Ka lura da shi, idan kudin da kashe yafi wannan, zan biya ka idan na dawo.'''
Sa'annan Yesu ya tambayi masanin shari'ar, "Me kake tunani? A cikin mutanen nan uku, wanene makwabcin wanda aka yi wa fashi da duka?" Sai ya amsa. "Wanda ya yi masa jinkai." Yesu ya gaya masa, "Kaima jeka kayi haka."