unfoldingWord 36 - Sakewar Kamanni
Kontuur: Matthew 17:1-9; Mark 9:2-8; Luke 9:28-36
Skripti number: 1236
Keel: Hausa
Publik: General
Eesmärk: Evangelism; Teaching
Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture
Olek: Approved
Skriptid on põhijuhised teistesse keeltesse tõlkimisel ja salvestamisel. Neid tuleks vastavalt vajadusele kohandada, et need oleksid arusaadavad ja asjakohased iga erineva kultuuri ja keele jaoks. Mõned kasutatud terminid ja mõisted võivad vajada rohkem selgitusi või isegi asendada või täielikult välja jätta.
Skripti tekst
Wata rana, Yesu ya dauki uku daga cikin almajiransa, Bitrus, Yakubu, da Yahaya. (Almajirin nan mai suna Yahaya ba shine wanda yayi wa Yesu baftisma ba.) Sun hau kan dutse mai tsawo domin su yi addu'a su kadai.
Da Yesu yana addu'a, sai fuskarsa tayi annuri (Haske) kamar rana kuma tufafinsa suka zama fari fat, fiye da yadda wani a duniya zai maishe su.
Sa'annan Musa da annabi Iliya suka bayyana. Wadannan mutane sun yi zama a duniya daruruwan shekaru kafin lokacin nan. Sun yi magana da Yesu game da mutuwarsa, wanda zai faru ba da dadewa ba a Urushalima.
Yayin da Musa da Iliya ke magana da Yesu, Bitrus yace wa Yesu, "Yana da kyau da muke a nan. Bari mu kafa bukkoki uku, daya na ka, daya na Musa, daya kuma na Iliya." Bitrus bai san abinda yake fada ba.
Yayin da Bitrus ke magana, girgije mai haske ta sauko ya lullube su sai murya daga girgijen ya ce, "Wannan shine dana wanda nake kauna. Ina farin ciki da shi. Ku saurare shi." Almajiran nan uku suka razana suka fadi kasa.
Sai Yesu ya taba su ya ce, "Kada ku ji tsoro. Ku tashi." Sa'anda suka duba kewaye, sai Yesu shi kadai ke wurin.
Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga dutsen. Sai Yesu yace masu, "Kada ku gaya wa kowa abinda ya faru anan tukunna. Bada dadewa ba, zan mutu in kuma sake rayuwa. Bayan haka, zaku iya fada wa mutane."