Επιλέξτε μια Γλώσσα

mic

Μερίδιο

Μοιράζομαι ένα σύνδεσμο

QR code for https://globalrecordings.net/script/ha/1237

unfoldingWord 37 - Yesu ya Tada Li'azaru daga Matattu

unfoldingWord 37 - Yesu ya Tada Li'azaru daga Matattu

Περίγραμμα: John 11:1-46

Αριθμός σεναρίου: 1237

Γλώσσα: Hausa

Κοινό: General

Σκοπός: Evangelism; Teaching

Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture

Κατάσταση: Approved

Τα σενάρια είναι βασικές οδηγίες για μετάφραση και ηχογράφηση σε άλλες γλώσσες. Θα πρέπει να προσαρμόζονται όπως είναι απαραίτητο για να είναι κατανοητές και σχετικές με κάθε διαφορετική κουλτούρα και γλώσσα. Ορισμένοι όροι και έννοιες που χρησιμοποιούνται μπορεί να χρειάζονται περισσότερη εξήγηση ή ακόμη και να αντικατασταθούν ή να παραλειφθούν εντελώς.

Κείμενο σεναρίου

Wata rana, Yesu ya sami sako cewa Li'azaru yana tsananin rashin lafiya. Li'azaru da yan'uwansa biyu mata, Maryamu da Marta, abokan Yesu ne na kusa. Sa'anda Yesu ya ji labarin, sai ya ce, "Wannan ciwon ba zai kare a mutuwa ba, amma domin daukakar Allah." Yesu ya na kaunar abokansa, amma ya jira har kwana biyu a inda ya ke.

Bayan kwana biyun sun wuce, Yesu ya ce wa almajiransa, "Bari mu koma Yahudiya." Almajiran suka amsa, ''Amma malam, ba da dadewa ba mutanen wurin sun so su kashe ka!" Yesu ya ce, "Abokin mu Li'azaru ya yi barci, kuma dole ne in tashe shi."

Almajiran Yesu suka amsa, "Mai gida, inda Li'azaru ya na barci, to ya zama masa mafi alheri." Sa'annan Yesu ya gaya masu afili, "Li'azaru ya mutu. Na yi murna da ba na nan a wurin, domin ku gaskanta da ni."

Sa'adda Yesu ya isa garin Li'azaru, Li'azaru ya riga ya mutu da kwana hudu. Marta ta fito waje ta sami Yesu, ta ce, "Maigida, inda kana nan, da dan'uwana bai mutu ba. Amma na gaskanta Allah zai ba ka duk abinda ka roka daga gare shi."

Yesu ya amsa, "Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskanta da ni zai rayu, ko da ma ya mutu. duk wanda ya gaskanta da ni ba zai taba mutuwa ba. Kin gaskanta da wannan?" Marta ta amsa, "I, Maigida! Na gaskanta kai ne Almasihu, Dan Allah."

Sa'annan Maryamu ta iso. Ta fadi a kaffafun Yesu, ta ce, "Maigida, da dai kana nan, da dan'uwana bai mutu ba." Yesu ya tambaye su, "Ina ku ka ajiye Li'azaru?" Suka gaya masa, "A kabari. Zo ka gani." Sa'annan Yesu ya yi kuka.

Kabarin kogo ne, da dutse da aka mirgina a gaban kofar. Sa'anda Yesu ya isa kabarin, ya gaya masu, "Ku mirgina dutsen." Amma Marta ta ce, "Kwana hudu ke nan da mutuwarsa. Za a yi mummunar wari."

Yesu ya amsa, "Ba na gaya ma ki cewa za ki ga daukakar Allah idan ki ka gaskanta ni ba?" Sai suka mirgina dutsen gefe.

Sai Yesu ya dubi sama ya ce, "Uba, na gode maka domin kana ji na. Na san ka na ji na kullum, amma na fadi haka saboda wadannan mutane da ke tsaye a nan, domin so bada gaskiya kai ka aiko ni." Sai Yesu yayi ihu, "Li'azaru, fito wuje!"

Sai Li'azaru ya fito waje! Yana nannade a likafani. Yesu ya ce masu, "Ku taimake shi cire likafanin ya tafi!" Yahudawa da yawa sun gaskanta da Yesu saboda wannan al'ajibi.

Amma shugabanin adinin na Yahudawan suka ji kyashi, sai suka taru domin su shirya yadda za su kashe Yesu da Li'azaru.

Σχετική πληροφορία

Λόγια Ζωής - Ηχητικά μηνύματα του ευαγγελίου σε χιλιάδες γλώσσες που περιέχουν μηνύματα βασισμένα στη Βίβλο για τη σωτηρία και τη χριστιανική ζωή.

Copyright and Licensing - GRN shares its audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?